Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 25

VOA Hausa

Kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da Rakonni da Tsagi da Kalhu da kuma Gi’ire, duk a cikin gundumar Gandi da ke karamar hukumar mulki ta Rabah, inda ‘yan bindigar da ba’a tantance adadinsu ba, suka kai harin bai daya a daren ranar Asabar, suka kuma kashe a kalla mutane 25.

Haka ma a makwanni ukku da suka gabata wasu yan bindiga suka sunkai irin wannan harin a kananan hukumomin Mulkin Isa da Gudu, yayin da ake hasashen yaduwar hare-haren ‘yan bindiga a makwabtan jihar, a dai-dai lokacin da jami’an soji suke ci gaba da fatattakar su daga jihar Zamfara.

Wannan harin na baya-bayan nan na zuwa ne ‘yan makwanni bayan da gwamnan jihar Sokoton Aminu Waziri Tambuwal, ya gudanar da wani taro da dukkan shugabannin hukumomin tsaro dake jihar ta Sokoto, ciki kuwa har da babban kwamandan shiyya ta 8 ta rundunar sojin Nijeriya da ke Sokoton.

Yanzu haka ana zaman dar-dar a garuruwa da dama a yankin gabashin jihar Sokoto saboda fargabar cewa za’a iya kai hari a kowane lokaci, yayin da wasu al’ummomi da dama suka fice daga garuruwansu.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...