Yan Bindiga Sun Kashe Dan Kasuwa a Bauchi

Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe wani dan kasuwa daga kauyen Balele da ke karamar hukumar Ningi a jihar Bauchi mai suna Chinonsi Ugwu.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindigar suka isa kauyen da misalin karfe 1:30 na daren Talata, inda suka rika harbin makamansu.

Wata majiya da ba a bayyana sunanta ba wacce ta zanta da ‘yan jarida ta ce ‘yan bindigar na tada fargaba da hargitsi a wasu al’ummomi da ke yankin.

Musamman ma sun kai hari gidan dan kasuwan mai shekaru 37 kuma sun harbe shi sau da dama a ciki da kai.Saboda tsoron kada a kai musu hari, babu wanda zai iya shiga tsakani sai washe gari, inda daga karshe aka kai wanda aka kashe zuwa asibiti tare da rakiyar jami’an ‘yan sanda.

Saboda tsoro, babu wanda ya iya fitowa sai washe gari, inda daga karshe aka kai wanda aka kashe zuwa asibiti tare da rakiyar jami’an ‘yan sanda.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...