Ya kamata mulki ya koma Kudancin Najeriya a 2023 – El-Rufai

NASIRU AHMAD EL-RUFAI

Bayanan hoto,
Gwamnan Kaduna Nasiru Ahmad El-Rufai

Gwamnan jihar Kaduna a Najeriya ya nemi a miƙa wa yankin kudancin ƙasar mulki a shekarar 2023 bayan wa’adin mulkin Shugaba Muhammadu Buhari.

Mallam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana haka ne cikin wata hira da yayi da BBC.

“Idan ka kalli yadda nake, ba na ɗaukar mutum yayi aiki tare da ni domin shiyyar da ya fito. Cancanta na ke dubawa, ina duba wanda idan aka ba shi amanar jama’a zai riƙe ta yadda ya kamata.”

Ya kuma ce, “A siyasar da ake yi a Najeriya, akwai tsarin da ake bi na karba-karba, inda kowa ya amince cewa idan arewa ta yi mulki shekara takwas, kudu za ta yi mulki shekara takwas.”

Ya ce duk da ba a rubuta tsarin karɓa-karɓan a tsarin mulki ba, amma kowane ɗan siyasa a ƙasar ya san da shi.

‘Shi yasa na fito na ce bayan Shugaba Buhari ya yi shekara takwas, ka da wani ɗan arewa ya nemi muƙamin. A bar ƴan kudu suma su sami shekara takwas.”

Da aka tambaye shi ko da gaske yana da ra’ayin tsayawa takarar shugabancin Najeriya, sai ya ce:

“Ana cewa ina son shugaban ƙasa tun ina ministan Abuja, amma ba na so. Wannan shirme ne.”

Ya kuma ci gaba da cewa Allah shi ke bayar da shugabanci, “ko kana so, ko ba ka so yana iya ba ka. Amma ni ban taɓa neman shugabancin Najeriya ba kuma babu wanda zai ce na taɓa nema.”

Batun rufe kasuwannin Kaduna

Tun da cutar korona ta bayyana a Najeriya, gwamnatoci sun ɗauki matakan killace al’umominsu a gida inda har ta kai sun kulle makarantu da wuraren aiki da kasuwanni.

A jihar Kaduna, duk da gwamnatin jihar kaduna ta sassauta matakan kullen da ta saka wa al’umar jihar, har yanzu ba ta buɗe wuraren ibada da kasuwanni da makarantu ba.

Wannan ne ya sa ƴan kasuwa ke ƙorafe-ƙorafe kan batun, suna cewa matakin gwamnan jihar na iya kassara su.

Amma gwamnan na Kaduna ya kare kansa daga zargin da ake yi cewa ya ƙi tausaya wa ƴan kasuwan.

“Su ƴan kasuwa suna cewa sun fara bara. Mun ji, amma gara kayi bara kana da rai da ka mutu.”

Ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta buɗe kasuwanni da wuraren ibada ne kawai bayan ta sha ƙarfin annobar.

Mallam Nasiru El-Rufai: “Bayan rufe jiha da muka yi kwana 75, sannu a hankali mun buɗe wasu sassan na rayuwa domin mu ga ko mutane za su yi biyayya ga dokokin da jami’an kiwon lafiya suka gindaya domin kare al’umma daga kamuwa da cutar ta korona.”

Ya koka da yadda mutane a jihar ba sa kiyaye wa kamar yadda aka buƙace su.

“Idan muka buɗe masallatai da kasuwanni, cunkoson da muke gani ana yi ƙaruwa zai yi ba raguwa ba. Kuma mutum ɗaya da ke da cutar na iya yaɗa ta ga dubban mutane.”

Ya kuma ce saboda yadda cutar ke kara bazuwa a jihar, gwamnati na iya mayar da hannun agogo baya.

“Yanzu ma abin da muke dubawa shi ne, ƙila mu rufe jihar domin yadda cutar ke ƙaruwa. Muna fargabar yana iya fin ƙarfin asibitocinmu. Ƙila su sake rufe jihar a koma gidan jiya.”

Ya kuma yi alƙawarin tallafa wa ƴan kasuwan idan komai ya koma dai-dai: “Za mu sami hanyoyin tallafa mu su bayan komai ya lafa, amma mutumin da ya riga ya mutu, ko wace irin kasuwanci yake yi ba zai amfane shi ba, sai dai ta lahira.”

Yaushe za a buɗe makarantu?

Duk da gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da ranakun da za a buɗe makarantu a ƙasar, gwamnan na Kaduna na ganin akwai sauran rina a kaba.

Ya ce gwamantinsa za ta yi nazari domin ta ga ko ya dace a sake buɗe makarantu a faɗin jihar:

“Muna nan muna dubawa. Akwai manyan shirye-shirye da za mu yi – idan ba haka ba, ba za mu buɗe su ba,” inji gwamnan.

Matsalar tsaro a kudancin Kaduna

Wani batu da ke jan hankalin mutane a Najeriya shi ne na rashin tsaro.

Yayin da jihohin arewa maso gabas ke fama da ayyuakn ta’addanci, su kuwa na arewa maso yammaci na fuskantar barazana ne daga ɓarayin daji da kuma masu satar mutane domin su karɓi kuɗin fansa.

Gwamna El-Rufai ya ce ƴan bindigan da ke kai hare-hare a kudancin jihar suna yin haka ne domin dalilai na tattalin arziki: Waɗannan ƴan bindiga su ne ke kashe-kashe da sace-sace a kudancin Kaduna.”

Ya kara da cewa, “abin da na lura shi ne wasu mutane na amfani da siyasa da addini ko ƙabilanci a dagula maganar.”

Da BBC ta tambaye shi su wane ne ke amfani da siyasa da addini, sai gwamnan ya ce:

“Akwai waɗanda mun kayar da su a zaɓe amma har yanzu sun kasa dangana, shi yasa suke son tayar da hankali. Sun rantse sai jihar nan an kasa mulkinta.”

Ya kuma ce akwai wasu kuma da suka kafa gaba da wasu al’umomin da ke zaune cikin jihar, har suna kiransu baƙi.

Ya ce akwai garuruwa kamar Zonkwa da Kafanchan da Zangon-Kataf da garuruwa da mutane daga wasu yankunan arewacin Najeriya kamar Kano da Bauchi da sauransu sun je kudancin Kaduna sun zauna.

“Akwai waɗanda suka tashi suna cewa waɗannan mutanen baƙi ne kuma sai sun bar wurin. An fara irin wannan tashin hankalin a jihar Kaduna tun 1980 da aka far wa mutanen Kasuwan Magani aka kashe mutum 11.”

Mallam Nasiru El-Rufai ya kare zargin da ake wa gwamnatinsa cewa ta kasa magance matsalar, inda ya ce ko a zamanin tsohon gwamna marigayi Patrick Yakowa irin wannan rikicin ya auku.

“Patrick Yakowa ɗan kudancin Kaduna ne, kuma mutanen yankin sun nuna irin wannan hali. Sun far wa mutane kuma sun kashe su.”

Ya kuma ce saboda matakan tsaron da ya riƙa ɗauka ne lamarin tsaron ya tsaya inda yake.

“Wadanda ke cewa abin ya fi ƙarfinmu ba su yi mana adalci ba. Abin da mutane ba su sani ba shi ne yadda muka hana ƙulle-ƙullen da wasu ke yi na far wa mutane su kashe su a jihar.”

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...