Hukumomi sun kama wata amarya ‘yar shekara 20 mai suna Amina Hassan daga karamar hukumar Mubi ta Arewa a jihar Adamawa bisa laifin cinna wa gidan mijinta wuta.
Amina ta ɗauki wannan matakin ne saboda kin rubuta mata takardar saki.
An ce ma’auratan sun kulla yarjejeniya kafin aurensu.
A cewar wasu rahotanni, Amina ta sanar da iyayenta cewa ba ta da sha’awar yin wannan auren kwanaki kadan kafin ɗaurin auren.
Duk da haka, iyayenta sun dage cewa dole ne a yi bikin aure saboda sun riga sun raba katunan gayyata.
Bayan an daura auren ne ta nemi taimakon wani boka don ya sa mijinta ya tsane ta ya sake ta.