Wata mata ta cinna wa gidan mijinta wuta saboda ya ƙi ya sake ta

Hukumomi sun kama wata amarya ‘yar shekara 20 mai suna Amina Hassan daga karamar hukumar Mubi ta Arewa a jihar Adamawa bisa laifin cinna wa gidan mijinta wuta.

Amina ta ɗauki wannan matakin ne saboda kin rubuta mata takardar saki.

An ce ma’auratan sun kulla yarjejeniya kafin aurensu.

A cewar wasu rahotanni, Amina ta sanar da iyayenta cewa ba ta da sha’awar yin wannan auren kwanaki kadan kafin ɗaurin auren.

Duk da haka, iyayenta sun dage cewa dole ne a yi bikin aure saboda sun riga sun raba katunan gayyata.

Bayan an daura auren ne ta nemi taimakon wani boka don ya sa mijinta ya tsane ta ya sake ta.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...