
Wasu mutane biyu da ake zarginsu da kasancewa manyan ƴan ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP ne sun mika kansu ga jami’an tsaro a jihar Yobe.
Ɗaya daga cikin mutanen kwararre ne wajen haɗa bam da ake ɗaurawa a jikin motar.
Wata majiyar jami’an tsaro ta fadawa kafar yaɗa labarai ta Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi cewa mutanen sun miƙa kansu ne ga dakarun sojan Bataliya ta 159 dake garin Geidam a jihar Yobe.
A cewar majiyar yan ta’addan da suka mika wuya su hada da Abu Umar da kuma Ismail Muhammad.
“majiyar dakarun soja ta bayyana Abu Umar a matsayin injiniya kuma kwararre wajen haɗawa da ɗana bom ɗin da ake makalawa a mota,” a cewar kafar ta Makama.
Majiyar ya kara da cewa yan ta’addan dake da masaniya wajen kera bom ɗin na da matsayi babba a kungiyar ta’addancin saboda rawar da suke takawa wajen kai manyan hare-hare kan jami’an tsaro.
Ya kara da cewa bayanan da za a samu daga yan ta’addan za su taimaka wajen gano wuraren da yan ta’addan ke amfani da su wajen haɗa bama-bamai.

