Wasu manyan ƴan ta’addar ƙungiyar ISWAP sun mika kansu ga jami’an tsaro

Wasu mutane biyu da ake zarginsu da kasancewa manyan ƴan ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP ne sun mika kansu ga jami’an tsaro a jihar Yobe.

Ɗaya daga cikin mutanen kwararre ne wajen haɗa bam da ake ɗaurawa a jikin motar.

Wata majiyar jami’an tsaro ta fadawa kafar yaɗa labarai ta Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi cewa mutanen sun miƙa kansu ne ga dakarun sojan Bataliya ta 159 dake garin Geidam a jihar Yobe.

A cewar majiyar yan ta’addan da suka mika wuya su hada da Abu Umar da kuma Ismail Muhammad.

“majiyar dakarun soja ta bayyana Abu Umar  a matsayin  injiniya kuma kwararre wajen haɗawa da ɗana bom ɗin da ake makalawa a mota,” a cewar kafar ta Makama.

Majiyar ya kara da cewa yan ta’addan dake da masaniya wajen kera bom ɗin na da matsayi babba a kungiyar ta’addancin saboda rawar da suke takawa wajen kai manyan hare-hare kan jami’an tsaro.

Ya kara da cewa bayanan da za a samu daga yan ta’addan za su taimaka wajen gano wuraren da  yan ta’addan ke amfani da su wajen  haɗa bama-bamai.

More from this stream

Recomended