Wani Matashi ɗan Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya a Yaƙin Rasha


Rahotanni sun tabbatar da mutuwar wani matashi ɗan Najeriya da ya tafi fagen yaƙi a ƙasar Rasha, inda ya rasa ransa yayin artabu.

Bayanan da aka samu sun nuna cewa matashin ya bar iyali, ciki har da ’ya’ya, waɗanda yanzu suke cikin alhini sakamakon rasuwarsa. Hotunansa tare da hotunan ’ya’yan da ya bari sun karade kafafen sada zumunta, lamarin da ya tayar da hankulan jama’a.

Lamarin ya sake jawo hankalin matasa kan haɗarin shiga yaƙe-yaƙe a ƙasashen waje, musamman ba tare da cikakken bayani da kariya ba.

Masu ruwa da tsaki na kira ga matasa da su yi taka-tsantsan, tare da yin tunani mai zurfi kafin yanke shawarar da za ta iya jefa rayuwarsu cikin hatsari.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]