Unicef: Cutar Pneumonia ta fi kisan kananan yara a Najeriya | BBC news

Pneumonia na yin kashe yara a duk kasa da dakika 39 a duniya

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Pneumonia na yin kashe yara a duk kasa da dakika 39 a duniya

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya ce a kowacce shekara cutar pneumonia na kashe kananan yara ‘yan kasa da shekaru biyar.

Rahoton hukumar kula da kananan yara ta Majalisar Dinkin Duniya Unicef ya ce Najeriya ce kasar da Pneumonia ta fi kashe kananan yara a duniya.

Rahoton ya nuna yadda ciwon ke sanadin kashe yara masu kasa da shekara biyar fiye da duk wani ciwo.

Alkalumman Unicef kan Cutar na 2018 sun nuna cewa kimanin yara 18 ke mutuwa duk sa’a daya sakamakon cutar Pneumonia.

Rahoton ya kuma ce daga cikin adadin yaran da suka mutu a 2018 a Najeriya, kashi 19 sun mutu ne sakamakon Pneumonia.

  • Tsohon minista ya karkatar da kudin kiwon lafiya
  • Amnesty ta gargadi gwamnatin Buhari kan kisan jama’a

Cutar da ta shafi huhu, Unicef ta ce matsaloli da suka shafi karancin abinci mai gina jiki da shakar hayakin itace da ake konawa wajen dafa abinci ne ke haifar da cutar ga yara kanana.

Baya ga Najeriya daga cikin kasashen da cutar ta fi tsanani, sun hada da Indiya da Pakistan da Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo da kuma Habasha.

A watan Janairu ne kungiyoyi da hukumomi za su gudanar da taron duniya a Spain domin tattauna cutar Pneumonia da ke kisan yara.

Jerin kasashen da cutar Pneumonia ta fi tsanani

Hukumar Unicef ta bayyana jerin kasashen da cutar pneumonia ta fi kisan yara ‘yan kasa da shekara biyar a 2018.

1. Nigeria 162,000

2. Indiya 127,000

3. Pakistan 58,000

4. Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo 40,000

5. Habasha 32,000

6. Indonesia 19,000

7. China 18,000

8. Chadi 18,000

9. Angola 16,000

10. Tanzania 15,000

11. Somalia 15,000

12. Nijar 13,000

13. Mali 13,000

14. Bangladesh 12,000

15. Sudan 11,000

Jimilla a duniya 802,000

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...