

Manoma a wasu sassan jihar Katsina sun shiga tsaka mai wuya sakamakon yadda Æ´an bindiga suke saka shanu suna lalata musu kayan amfanin gona.
Manoman sun bayyana da zarar kayi korafi Æ´an bindiga ka iya harbe mutum nan take.
Rahotanni sun nuna cewa manoman suna kwashe amfanin gonar su duk da cewa bai gama karasawa domin gujewa asara.
Garuruwan da suke ƙaramar hukumar Sabuwa na daga cikin wuraren da lamarin yafi kamari.
Wasu mazauna garin Dugun Mu’azu sun koka kan yadda hukumomi su gaza kawo musu É—auki kan halin da suka samu kansu a ciki.