Tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim El-Hassan Kwami, ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.
Marigayin wanda shi ne Sarkin Sudan na Kwami, ya taba rike mukamin kwamishina a jihar tare da yin aiki a Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa har zuwa matsayin babban jami’i.
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana alhininsa kan rasuwar marigayin tare da jajanta wa iyalansa da al’ummar jihar.
A wata sanarwa da Darakta Janar na Harkokin Yaɗa Labarai na Gidan Gwamnatin Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya ce marigayin ya kasance jajirtaccen ma’aikacin gwamnati wanda ya gudanar da aikinsa cikin ƙwarewa da gaskiya.
Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin tare da sanya shi a Aljannatul Firdausi.
Tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai Na Gombe, Ibrahim El-Hassan Kwami Ya Rasu

