Tinubu ya naɗa shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa da sakataren gwamnatin tarayya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya naɗa kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa.

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, Ibrahim Hassan Hadejia shi ne zai kasance mataimakin shugaban ma’aikatan fadar ta shugaban kasa.

Har ila yau Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan jihar Benue, George Akume a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya.

Wannan ne naɗe-naɗe na farko da shugaban kasar ya fara yi tun bayan da aka rantsar da shi a ranar Litinin 29 ga watan Mayu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]