Tinubu ya naɗa shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa da sakataren gwamnatin tarayya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya naɗa kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa.

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, Ibrahim Hassan Hadejia shi ne zai kasance mataimakin shugaban ma’aikatan fadar ta shugaban kasa.

Har ila yau Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan jihar Benue, George Akume a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya.

Wannan ne naɗe-naɗe na farko da shugaban kasar ya fara yi tun bayan da aka rantsar da shi a ranar Litinin 29 ga watan Mayu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]