Tinubu: Mun Fitar Da Miliyoyin ’Yan Najeriya Daga Talauci



Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa shirye-shiryen tallafin rayuwa da gwamnatinsa ta aiwatar sun taimaka wajen fitar da miliyoyin ’yan Najeriya daga kangin talauci.

Tinubu, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya wakilta a bikin Ranar Ma’aikata ta 2026 da aka gudanar a Dandalin Eagles Square da ke Abuja, ya ce gidaje miliyan 15 da ke cikin mawuyacin hali sun amfana da tallafin kuɗi, inda kimanin mutane miliyan 7.5 suka fita daga talauci.

Ya kuma ce manyan ayyukan gine-gine da gwamnati ke yi sun samar da ayyukan yi ga sama da mutum 600,000 a faɗin ƙasar, ciki har da aikin hanyar Legas zuwa Kalaba da bututun iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano.

Dangane da walwalar ma’aikata, shugaban ya ce an fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi, tare da biyan bashin fansho da dawo da gratuity tun daga Janairu 2026.

Haka kuma, ya bayyana cewa sama da ma’aikata 800,000 daga ɓangaren da ba na hukuma ba sun shiga shirin micro pension, yayin da ƙananan da matsakaitan masana’antu ke cin gajiyar tallafin Naira biliyan 200.

A ɓangaren noma kuwa, Tinubu ya ce gwamnati na ƙoƙarin inganta harkar noma da kuma kare manoma ta hanyar tura jami’an Agro-Rangers 10,000 a jihohi 19.

A ƙarshe, ya buƙaci ƙungiyoyin ƙwadago su rungumi tattaunawa maimakon yajin aiki, yana mai cewa “yajin aiki ya zama mafita ta ƙarshe, ba ta farko ba.”

More from this stream

Recomended