Najeriya da Turkiyya sun amince da kafa babbar cibiyar horon soji a Najeriya, a wani ɓangare na ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.
An cimma wannan yarjejeniya ne yayin wata tattaunawar diplomasiyya tsakanin ministocin tsaron ƙasashen biyu a gefen wani taron diplomasiyya na shekarar 2026.
A ƙarƙashin yarjejeniyar, dakarun tsaron Najeriya za su rika samun horo a fannoni daban-daban, ciki har da yaƙi da ta’addanci, tattara bayanan sirri, amfani da jirage marasa matuƙa, da kuma cire abubuwan fashewa da aka dasa. Haka kuma za a horar da su kan ayyukan kiyaye zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya.
Najeriya dai ta dade tana neman haɗin kai da taimakon ƙasashen waje wajen yaƙi da matsalolin tsaro, musamman ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindiga masu ɗauke da makamai.
A watan Fabrairu, Amurka ta tura dakaru 200 zuwa Najeriya domin horas da sojojin ƙasar da kuma taimaka musu da bayanan sirri.
Najeriya Da Turkiyya Sun Amince Da Kafa Cibiyar Horon Soji

