Sojoji Sun Lalata Cibiyar Ƙera Makamai Ta Haram A Kebbi



Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun gano tare da lalata wata haramtacciyar cibiyar ƙera makamai a jihar Kebbi.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar sashe na 2, Laftanar Kanal Aliyu Danja ya fitar, ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri.

Ya ce dakarun sun kutsa wurin da ake zargin ana amfani da shi wajen ƙerawa da safarar makamai masu alaƙa da ayyukan ta’addanci.

A cewarsa, sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyar na gida tare da kama wasu mutane biyu da ake zargin masu ƙera da safarar makamai ne.

Rundunar ta ce an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, domin dakile hanyoyin samar da makamai ga ƙungiyoyin masu aikata laifuka a yankin Arewa maso Yamma.

Ta ƙara da cewa ana ci gaba da tsare waɗanda aka kama domin gudanar da bincike kan sauran mutanen da ake zargi da hannu a lamarin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]