Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu Æ´an ta’adda biyu a Æ™auyen Kana dake Æ™aramar hukumar Biu ta jihar Borno.
A wata sanarwa ranar Asabar rundunar sojan ta ce an kashe Æ´an ta’addar ne a ranar 19 ga watan Afrilu.
Rundunar sojan ta ce dakarunta sun yi arangama da Æ´an ta’addar a wajejen Æ™auyen Nguma ta kara da cewa an gano babur É—aya da kekuna 6 sai bindiga Æ™irar AK-47 da kuma sauran kayayyaki da aka yi watsi da su.
A kuma wani samamen na daban dakarun sojan na Najeriya sun kai samame a ƙauyen Abuni dake ƙaramar hukumar Awe ta jihar Nasarawa kan wasu maɓoyar bata gari inda aka gano bindigogi.
An samu nasarar gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 a gidan wani da ake kira Abdullahi Musa tare da kama ƙarin wasu mutane.