Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 18 A Dajin Sambisa

Jami’an rundunar sojan Najeriya ta Operation Hadin Kai sun kai farmaki kan wata maboyar yan Boko Haram dake surkukin dajin Sambisa a karamar hukumar Bama ta jihar Borno inda suka kashe mutane 18.

A cewar wakilin jaridar Daily Trust sojojin sun samu kwararan bayanan sirri kan sabon sansanin mayakan na Boko Haram inda suke haduwa tare da kitsa yadda za su kai hari yankunan Sheutari da kuma Mutari.

LWata majiya dake rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta na 21 Brigade Task Force dake Bama da hadin gwiwar jami’an Civilian JTF su ne suka kai farmaki maboya.

Shima wani masani kan yaƙin dake faruwa a yankin arewa maso gabas Zagazola Makama ya tabbatar da kai farmakin.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...