
Malamin ya kuma ce, wadanda suka fahimci cewa shi ne ya kirkiri kalaman batanci ga annabi Muhammadu S.A.W da ake zarginsa da yi, sun yi wa kalaman nasa gurguwar fahimta ne.
“Wadannan maganganu idan daga ni ne, to duk duniya yau ta ji, ina gaggauta janye su da tuba akan su” malamin ya fada a cikin sanarwar.
To sai dai duk da haka malamin ya dage akan cewa akasarin maganganun da ya fada suna cikin litattafai ne ba shi ba ne ya kirkire su, dalili ke nan da ya ta’allaka tubar ta shi bisa sharadin idan har shi ne ya kirkiro su.
“Idan wannan maganganu miyagun daga ni suke, kirkirar su na yi babu su a litattafan hadisi, ai ko lalle wannan ya isa babban laifi da zunibi da ya wajaba in gaggauta tuba, ba ma sai wani wani ya tilasta ni ba. Wanda kuma ya tilasta ni kan wannan in har daga ni ne, to kuwa ban da masoyi irin sa” in ji Abduljabbar.
Lamarin neman afuwar da Shehin malamin ya yi dai na zuwa ne bayan sa’o’i 24 da fafatawa a wata mukabala tsakanin Sheik Abduljabbar Nasiru da wasu shehunan malamai a Jihar Kano, da gwamnatin jihar ta shirya ta kuma jagoranta.
Daga karshe dai malamin ya yi kira ga al’umman musulmi da su hada kai su kuma mike tsaye domin tabbatar da cewa ba a rusa addininsu na musulunci ba.
A wani bangare kuma, wani dan Sheik Abduljabbar Nasiru ya nemi afuwan al’umman musulmi a kafar Facebook bayan rashin gamsuwa da bayanin da mahaifinsa ya yi game da zargin da aka yi masa na batanci ga fiyayyen hallita.
Idan ana iya tunawa dai, a ranar Asabar da ta gabata ce gwamnatin jihar Kano ta shirya mukabala tsakanin malamin da wasu shehunan malamai daga bangarorin akida daban-daban inda suka tafka muhawar kan kalaman na Sheik Abduljabbar.
Daga karshen mukabalar dai, alkalin da ya jagoranci muhawarar, Farfesa Salisu Shehu, ya yanke hukuncin cewa, malam Abduljabbar ya gaza amsa dukkan tambayoyin da aka yi masa inda daga bisani gwamnatin Kano ta fara shirin gurfanar da malamin a gaban kuliya, kan zargin kalaman batanci da kuma na tunzura al’umma.
(VOA Hausa)