Sai doka ta yi aiki game da kisan da aka yi wa Ummita, in ji Ganduje

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta tabbatar da ganin shari’ah ta yi aikinta a batun kashe Ummukhulthum Sani Buhari, matashiyar da ake zargin wani dan China da aikatawa.

Dr. Abdullahi Umar Ganduje yayin wani jawabi a fadar gwamnatin jihar ya ce “Zub da jini (ne, don haka) dole maganar shari’ah ta shigo” kuma sai doka ta yi aikinta.

Ya ce tuni suka sa aka kama mutumin da ake zargi Mista Geng Quanrong, bayan mutane sun damke shi a gidansu marigayiyar ranar Juma’a.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne ran Juma’a da dare, inda Geng Quanrong dan shekara 47 ya kutsa kai gidansu Ummita a unguwar Kabuga cikin karamar hukumar Gwale.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce tana ci gaba da gudanar da bincike, inda ta mai da batun zuwa babban sashen binciken manyan laifuka bangaren kisan kai.

Mahaifiyar Ummita, Hajiya Lami Sani Buhari ta ce mutumin da ake zargi da kashe ‘yarta ya sha zuwa gidansu yana neman ganin Ummita, amma ba ta son fitowa.

Ta ce a ranar da lamarin ya faru, É—an Chinan da ake zargi ya sake zuwa gidan da daddare inda ya yi ta buga musu kofa, abin da ya tilasta wa mahaifiyar bude masa kofa, don jin abin da ke tafe da shi.

Uwar ta ce Mista Geng ya bangaje ta, ya kutsa kai cikin dakin Ummita, kuma da ganin ta sai ya zare wuka ya yi ta caka mata.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...