Gwamnatin Najeriya ta fara shirin dawo da ‘yan kasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, sakamakon karuwar fargabar yiwuwar hare-hare kan baki a ƙasar.
Ministar harkokin wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta bayyana cewa akalla mutum 130 ne suka riga suka yi rijista domin shiga shirin, inda ta ce ana sa ran adadin zai ci gaba da ƙaruwa.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, ministar ta ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nuna matuƙar damuwa kan hare-haren da ake kai wa, tare da yin Allah wadai da tashin hankali, zanga-zangar ƙin jinin baƙi, da kalaman ƙiyayya.
Ta kuma ƙara da cewa an kashe ‘yan Najeriya biyu a hare-hare daban-daban da jami’an tsaro suka aiwatar, inda ta jaddada cewa gwamnatin Najeriya na neman a yi adalci.
A nasa bangaren, Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya yi Allah wadai da hare-haren, amma ya gargadi baki da ke zaune a ƙasar da su mutunta dokokin ƙasar.
Najeriya Ta Fara Shirin Mayar Da ‘Yan Kasarta Daga Afirka Ta Kudu

