Najeriya Ta Fara Shirin Mayar Da ‘Yan Kasarta Daga Afirka Ta Kudu



Gwamnatin Najeriya ta fara shirin dawo da ‘yan kasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, sakamakon karuwar fargabar yiwuwar hare-hare kan baki a ƙasar.

Ministar harkokin wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta bayyana cewa akalla mutum 130 ne suka riga suka yi rijista domin shiga shirin, inda ta ce ana sa ran adadin zai ci gaba da ƙaruwa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, ministar ta ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nuna matuƙar damuwa kan hare-haren da ake kai wa, tare da yin Allah wadai da tashin hankali, zanga-zangar ƙin jinin baƙi, da kalaman ƙiyayya.

Ta kuma ƙara da cewa an kashe ‘yan Najeriya biyu a hare-hare daban-daban da jami’an tsaro suka aiwatar, inda ta jaddada cewa gwamnatin Najeriya na neman a yi adalci.

A nasa bangaren, Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya yi Allah wadai da hare-haren, amma ya gargadi baki da ke zaune a ƙasar da su mutunta dokokin ƙasar.

More from this stream

Recomended