Mutum ya jikkata bayan da wata mota ta fado daga gadar sama a Lagos

Mutum guda ya jikkata a ranar Asabar lokacin da wata babbar mota dake dauke da kayan dab’i ta faɗa cikin wani rami bayan da ta fado daga kan gadar Oshodi a birnin Lagos.

An ruwaito cewa birki ya kwace wa motar a lokacin da ta ke saukowa daga gadar ta Oshodi bayan da ta fito daga hanyar Oshodi-Oke  zuwa mile 2.

A wata sanarwa da aka fitar, Adebayo Taofiq mai magana da yawun hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Lagos, LASTMA ya ce an ceto wanda ya jikkata aka kuma garzaya da shi ya zuwa asibitin dake kusa domin samun kulawar likitoci.

Taofiq ya ce an kama direban motar an mika shi hannun jami’an yan sanda na caji  ofis din Makinde domin fadada bincike tare da gano dalilin shanyewar birkin motar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]