Mutum 4 sun mutu yayin da ramin haƙar ma’adanai ya rufta da su a Bauchi

Aƙalla mutane hudu ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a karamar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.

Lamarin ya faru ne a Yadagungume da ke gundumar Burra ranar Asabar.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho, inda ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa a ranar da wani ya kai rahoton faruwar lamarin.

Ya ce da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda reshen Ningi ya tara mutanensa zuwa inda ake hakar ma’adinan, inda aka kwashe gawarwakin wadanda suka mutu aka kai su asibiti.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]