Mutum 4 sun mutu yayin da ramin haƙar ma’adanai ya rufta da su a Bauchi

Aƙalla mutane hudu ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a karamar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.

Lamarin ya faru ne a Yadagungume da ke gundumar Burra ranar Asabar.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho, inda ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa a ranar da wani ya kai rahoton faruwar lamarin.

Ya ce da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda reshen Ningi ya tara mutanensa zuwa inda ake hakar ma’adinan, inda aka kwashe gawarwakin wadanda suka mutu aka kai su asibiti.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]