Mutum 4 sun mutu yayin da ramin haÆ™ar ma’adanai ya rufta da su a Bauchi

Aƙalla mutane hudu ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a karamar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.

Lamarin ya faru ne a Yadagungume da ke gundumar Burra ranar Asabar.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho, inda ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa a ranar da wani ya kai rahoton faruwar lamarin.

Ya ce da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda reshen Ningi ya tara mutanensa zuwa inda ake hakar ma’adinan, inda aka kwashe gawarwakin wadanda suka mutu aka kai su asibiti.

More News

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...