Mutum Ɗaya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya, Bakwai Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Bam A Zamfara



Mutum ɗaya ya rasa ransa yayin da wasu bakwai suka samu raunuka bayan wani bam na hannu (IED) ya fashe a kan hanyar Bagega zuwa Anka da ke Ƙaramar Hukumar Anka a Jihar Zamfara.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wata motar fasinja kirar Golf 3 Wagon da ke ɗauke da matafiya daga Bagega zuwa Anka ta taka bam ɗin da ake zargin wasu ‘yan bindiga sun dasa a hanyar.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara, Yazid Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce jami’an tsaro tare da sojoji sun garzaya wurin domin tantance halin da ake ciki, tabbatar da tsaro da kuma sake buɗe hanyar ga masu amfani da ita.

Ya kuma jaddada aniyar hukumomin tsaro na ci gaba da yaƙi da ‘yan bindiga da sauran masu tayar da zaune tsaye a jihar, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin inganta ayyukan tsaro.

More from this stream

Recomended