Me ya sa aka hana yin tashe a Kano?

JIhar Kano

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Yayin da ake cikin kwanaki na tsakiyar watan azumin Ramadana, tuni tashe, wanda ke daya daga cikin al’adun da suka shahara a kasar Hausa ya kankama a sassa daban-daban na jihohin arewacin Najeriya da ma kasashe masu makwaftaka.

Sai dai a jihar Kano wadda take a matsayin daya daga cikin manyan yankuna na kasar Hausa, abin ba haka yake ba.

Domin kuwa kamar yadda ta faru a wasu shekarun baya, a wannan karo ma hukumomi a jihar sun haramta gudanar da wannan al’ada mai dinbin tarihi.

A yanzu haka tuni rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar ta Kano ta ce za ta dauki tsattsauran mataki kan duk wanda aka kama ya taka dokar hana yin tashe a jihar.

DSP Haruna Kyawa, mai magana da yawun rundunar ‘yansanda a jihar ya ce jami’an ‘yan sanda na yin sintiri a cikin dare domin tabbatar da cewa ba a bari masu neman tayar da fitina sun cimma burinsu ba.

Ya ce “ba wai tashen ne laifi ba, a’a. Amma bata gari da suke bin ‘yan tashen suke fakewa da haka suke yin kwace da sauran miyagun laifi shi ne ba ma so.”

Ya kuma kara da cewa rundunar za ta rika sintiri a lungu da sako na jihar daga lokacin sallar magariba zuwa karfe goma na dare don kama masu karya doka.

A lokacin tashe dai yara da manyan mata da maza ne kan yi shiga iri-iri na domin aikewa da sakonin daban-daban da kuma nishadantar da mutane ta hanyar barkwanci da kuma kade-kade da wake-wake.

[ad_2]

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...