Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din N30,000.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, a wasu tattaunawa daban-daban a Abuja, sun ce ci gaba da biyan kudaden alawus-alawus din na kowane wata na kara zama abin damuwa.

Mista Francisco Noah, wanda ya ci gajiyar sashen N-Teach na Batch C1, wanda ke koyarwa a makarantar makiyaya da ke garin Keffi a jihar Nasarawa ya ce jinkirin da aka samu ya sa ya daina zuwa makarantar.

Ya ce yanayin yana da matukar wahala a gare shi domin wani lokacin kudin sufuri yakan yi masa wuya ya je makarantar makiyayan.

Noah wanda ya nuna rashin jin dadinsa kan jinkirin ya ce karo na karshe da ya samu alawus din shi ne a watan Nuwambar 2022.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...