Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din N30,000.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, a wasu tattaunawa daban-daban a Abuja, sun ce ci gaba da biyan kudaden alawus-alawus din na kowane wata na kara zama abin damuwa.

Mista Francisco Noah, wanda ya ci gajiyar sashen N-Teach na Batch C1, wanda ke koyarwa a makarantar makiyaya da ke garin Keffi a jihar Nasarawa ya ce jinkirin da aka samu ya sa ya daina zuwa makarantar.

Ya ce yanayin yana da matukar wahala a gare shi domin wani lokacin kudin sufuri yakan yi masa wuya ya je makarantar makiyayan.

Noah wanda ya nuna rashin jin dadinsa kan jinkirin ya ce karo na karshe da ya samu alawus din shi ne a watan Nuwambar 2022.

More News

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi Æ™arancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...