Wike ya ziyarci shugaban jam’iyar APC

Nyesom Wike ministan babban birnin tarayya Abuja a ranar Talata ya ziyarci shugaban jam’iyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda a gidansa dake Abuja.

Har ya zuwa lokacin wallafa wannan labarin babu wata sanarwa da ta bayyana dalilin ganawar ta su.

Sai dai ziyarar na zuwa ne dai-dai lokacin da ake cigaba da jayayya da cece-ku-ce kan yadda aka tantance yan takarar jam’iyyar APC musamman yan majalisar dokokin jihar ta Ribas.

Kwamitin tantance yan takarar da uwar jam’iyar ta tura jihar ya amince da takarar yan takara 33 a yayin da aka soke takarar 65 gabanin zaɓen fidda gwanin jam’iyar.

Jumullar yan takara 98 ne suka sayi fom din takarar kujeru 32 na majalisar dokokin jihar

Kwamitin tantacewar dake ƙarƙashin jagorancin tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Muraina Ajibola ya bayyana dalilai daban-daban da suka saka su soke takarar wasu daga cikin ƴan takarar.

More from this stream

Recomended