Magoya Bayan Jam’iyyar APC Sun Yi Dandazo A Ofishin INEC A Kano

—VoA Hausa

Magoya bayan jam’iyyar APC mai mulki a Kano, sun yi tattaki zuwa ofishin hukumar zabe ta INEC, don nuna rashin gamsuwarsu da sakamakon zaben gwamna.

A farkon makon nan hukumar ta INEC ta ayyana dan takarar NNPP, Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida-gida, a matsayin wanda ya lashe zaben Gwamna a jihar, wanda aka yi a ranar 18 ga watan Maris a Najeriya.

Rahotanni sun yi nuni da cewa, yayin tattakin, an ga magoya bayan dan takarar APC, Nasiru Gawuna dauke da kwalaye da aka yi rubutu iri-iri suna waka suna dosar ofishin na INEC.

“Zaben jihar Kano bai kammalu ba,” wani daga cikin masu tattakin ya ce a wani hoton bidiyo da gidan Rediyon Freedom ta watsa kai-tsaye a shafinsa na Facebook.

Hukumar INEC ta ce Abba na NNPP ya samu kuri’a 1,019, 602 yayin da Gawuna ya samu 890,705.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...