Kotun Kolin Najeriya Za Ta Yanke Hukuncin Zaɓen Shugaban Ƙasa Ranar Alhamis

Kotun Koli ta saka ranar Alhamis domin yanke hukunci kan daukaka karar da Atiku Abubakar ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyar PDP a zaɓen da ya wuce da kuma Peter Obi na jam’iyar LP suka shigar gabanta.

Atiku da Obi na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Faburairu da ya bawa, Bola Ahmad Tinubu na jam’iyar APC nasara.

Daraktan yaɗa labarai kotun, Dr Festus Akande shi ne ya tabbatar da haka a ranar Laraba,

A ranar 9 ga watan Satumba ne kotun sauraron kararrakin zaɓen shugaban ƙasa ta kori karar da ƴan takarar biyu suka shigar saboda rashin hujjoji.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]