Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Bulala 20 Saboda Ya Saci Kaza

Wata kotun Musulunci a unguwar Ɗanbare da ke Kano ya yanke wa wani matashin mai suna Nazifi Hassan hukuncin bulala ashirin saboda ya saci kaza.

Bayan yanke masa wannan hukuncin, alkalin ya yi amfani da wannan damar wajen yi wa mai laifin nasiha tare da umurtar sa da ya mayar da kazar zuwa ga mai ita.

Mai laifin bai musa zargin da aka yi masa ba, yana mai cewa kwadayi ne ya ɗebe shi ya yi wannan aika-aika

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]