Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Bulala 20 Saboda Ya Saci Kaza

Wata kotun Musulunci a unguwar Ɗanbare da ke Kano ya yanke wa wani matashin mai suna Nazifi Hassan hukuncin bulala ashirin saboda ya saci kaza.

Bayan yanke masa wannan hukuncin, alkalin ya yi amfani da wannan damar wajen yi wa mai laifin nasiha tare da umurtar sa da ya mayar da kazar zuwa ga mai ita.

Mai laifin bai musa zargin da aka yi masa ba, yana mai cewa kwadayi ne ya ɗebe shi ya yi wannan aika-aika

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]