Kotu ta ce Abdullahi Sule ba shi ne ya lashe zaɓen Nasarawa ba

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Nasarawa ta bayyana Rt.Hon Davematics David E Ombugadu na PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Nasarawa da aka gudanar a watan Maris.

Kwamitin mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Ezekiel Ajayi, yayin da yake yanke hukuncin ta hanyar zurfafa bincike, ya ce Emmanuel Ombudagu na jam’iyyar PDP ne ya lashe zaben.

Ezekiel ya ci gaba da cewa mai shigar da kara ya iya tabbatar da hujjar sa ba tare da wata shakka ba kan zargin yin zabe, datse kuri’u, da dai sauran wasu kura-kurai.

Ku tuna cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Lafiya, ta bayyana Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar Nasarawa a watan Maris.

Farfesa Ishaya Tanko, jami’in zabe na INEC ya bayyana cewa dan takarar APC ya samu kuri’u 347,209 inda ya doke abokin hamayyarsa David Ombugadu, dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 283, 016.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...