Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Nasarawa ta bayyana Rt.Hon Davematics David E Ombugadu na PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Nasarawa da aka gudanar a watan Maris.
Kwamitin mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Ezekiel Ajayi, yayin da yake yanke hukuncin ta hanyar zurfafa bincike, ya ce Emmanuel Ombudagu na jam’iyyar PDP ne ya lashe zaben.
Ezekiel ya ci gaba da cewa mai shigar da kara ya iya tabbatar da hujjar sa ba tare da wata shakka ba kan zargin yin zabe, datse kuri’u, da dai sauran wasu kura-kurai.
Ku tuna cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Lafiya, ta bayyana Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar Nasarawa a watan Maris.
Farfesa Ishaya Tanko, jami’in zabe na INEC ya bayyana cewa dan takarar APC ya samu kuri’u 347,209 inda ya doke abokin hamayyarsa David Ombugadu, dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 283, 016.