Ƙasar Koriya ta Arewa ta harba wani makami mai linzami mai matsakaici zango a gabashin yankin.
Kamar yadda kanfanin dillancin labaran Koriya ta Kudu Yonhap ya rawaito, a labaran da aka samu daga ma’aikatar tsaron ƙasar Koriya ta Arewa ta harba makamai masu linzamin ne daga garin Wonsan zuwa gabashin gulf ɗin yankin.
An bayyana cewar ta harba makaman ne da misalin karfe 09 da minti 06 agogon ƙasar. Kawo yanzu dai ba’a samu cikakkiyar bayani game abubuwan da makaman suka ƙunsa ba.