Katsina: ’Yan Fashi Sun Kai Hari A Kauyen Dinkawa, Sun Sace Mutane Biyar, Sun Yi Fashin Shanu

’Yan fashi sun kai hari a daren Lahadi a kauyen Dinkawa dake karamar hukumar Charanchi a jihar Katsina, inda suka sace mutane biyar sannan suka yi fashin wasu shanu.

Wani masani kan harkokin tsaro, Bakatsine, ya bayyana lamarin a wani rubutu a shafin X a ranar Litinin.

A cewar Bakatsine, harin ya shafi zirga-zirgar hanyoyi a kan hanyar Kano–Katsina, wadda aka rufe bayan sallan Isha.

“Jiya da daddare, ’yan fashi sun kai hari a kauyen Dinkawa a karamar hukumar Charanchi, jihar Katsina, inda suka sace mutane biyar kuma suka yi fashin wasu shanu. Rashin tsaro a yankin Kankia na kara tsananta, an ruwaito cewa hanyar Kano–Katsina ta rufe bayan sallan Isha,” in ji shi.

A halin yanzu, hukumomi ba su fitar da wani bayani na hukuma game da lamarin ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]