Katsina: ’Yan Fashi Sun Kai Hari A Kauyen Dinkawa, Sun Sace Mutane Biyar, Sun Yi Fashin Shanu

’Yan fashi sun kai hari a daren Lahadi a kauyen Dinkawa dake karamar hukumar Charanchi a jihar Katsina, inda suka sace mutane biyar sannan suka yi fashin wasu shanu.

Wani masani kan harkokin tsaro, Bakatsine, ya bayyana lamarin a wani rubutu a shafin X a ranar Litinin.

A cewar Bakatsine, harin ya shafi zirga-zirgar hanyoyi a kan hanyar Kano–Katsina, wadda aka rufe bayan sallan Isha.

“Jiya da daddare, ’yan fashi sun kai hari a kauyen Dinkawa a karamar hukumar Charanchi, jihar Katsina, inda suka sace mutane biyar kuma suka yi fashin wasu shanu. Rashin tsaro a yankin Kankia na kara tsananta, an ruwaito cewa hanyar Kano–Katsina ta rufe bayan sallan Isha,” in ji shi.

A halin yanzu, hukumomi ba su fitar da wani bayani na hukuma game da lamarin ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]