Jiragen Ruwa 28 Dauke Da Mai Da Kayan Masarufi Za Su Iso Tashoshin Jiragen Ruwa Na Lagos

Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa (NPA) ta sanar da cewa akalla jiragen ruwa 28 ne ake sa ran za su iso tashoshin jiragen ruwa na jihar Lagos tsakanin ranar 19 zuwa 28 ga watan Fabrairu, 2026.

Sanarwar na kunshe ne a cikin sabon rahoton matsayin zirga-zirgar jiragen ruwa da hukumar ta fitar a ranar Alhamis a Lagos.

A cewar hukumar, daga cikin jiragen da ake sa ran za su iso, guda 20 jiragen dauke suke da kwantena masu dauke da kayayyaki iri-iri, yayin da sauran guda takwas ke dauke da danyen mai, dizal, hadadden man fetur, man jiragen sama da sauran kayayyaki.

Hukumar ta kuma bayyana cewa jiragen ruwa 12, ciki har da tankokin mai, sun riga sun isa tashar Apapa, Tin Can Island da Lekki Deep Sea Port, inda suke jiran a ba su damar sauke kaya.

Kayayyakin da wadannan jirage suka kawo sun hada da taki na urea, man jiragen sama, alkama mai yawa, fetur, kwantena da sauran kayayyaki.

Bugu da kari, NPA ta ce a halin yanzu jiragen ruwa 18 na sauke kayansu a tashoshin jiragen ruwan, inda ake sauke kaya kamar takin urea, gypsum, dizal, danyen mai, alkama, manyan motoci da sauran kayayyaki.

Hukumar ta bayyana cewa yawan zirga-zirgar jiragen ruwa da ake gani a tashoshin jiragen ruwan Lagos na nuna yadda harkokin shigo da kaya ke ci gaba da gudana ba tare da tsaiko ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]