
Kwamitin zartarwa na jam’iyar PDP ya gudanar da wani taron gaggawa a hedkwatar jam’iyar dake Abuja.
Taron na zuwa ne bayan da a yan kwanakin nan wasu jiga-jigan yan siyasa suka fice daga jam’iyar ciki har da gwamna mai ci.
Rikicin cikin gida da jam’iyar ke fama da shi na cigaba da kamari a dai-dai lokacin da ake tunkarar zabukan shekarar 2027.
A ranar 23 ga watan Afrilu gwamnan jihar Delta, Sheriff Obevwori da kuma tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa suka sauya sheka ya zuwa jam’iyar APC daga PDP.
Shima mataimakin gwamnan jihar da yan majalisar jiha da dukkanin shugabannin kananan hukumomi sun sanar da sauya shekarar ta su ya zuwa APC.
Ana sa ran shugabannin jam’iyar na PDP za su sanar da kwamitin riko da zai jagoranci jam’iyar a jihar Delta.