
Jam’iyyar APC ta ayyana Jamilu Isyaku Gwamna a matsayin wanda zai yi mata takarar gwamnan jihar Gombe a zaben shekarar 2027.
An ayyana Gwamna ne biyo bayan zaben fitar da gwani da aka gudanar a faɗin jihar.
Tun da farko gabanin zaɓen fitar da gwani gwamnan jihar, Inuwa Yahaya da kuma masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC a jihar ta Gombe sun fitar da sunan Gwamna a matsayin ɗantakarar maslaha da zai yi wa jam’iyyar takara. Sai dai wasu daga cikin ƴan takarar sun nuna rashin amincewarsu da haka.
Da yake sanar da sakamakon zaben, shugaban kwamitin zaɓen fitar da gwani na yan takarar gwamna a jihar, Sanata Sani Abubakar Danladi ya ce an gudanar da zaɓen ne kamar yadda dokar zaɓe ta shekarar 2022 ta tanada da kuma kundin sharudan hukumar INEC da jam’iyar APC.
Ya bayyana cewa jumullar masu kaɗa kuri’a 556,081 aka tantance domin kaɗa kuri’a a zaben da aka gudanar a ƙananan hukumomin jihar 11.
Gwamna ya samu nasara da kuri’a 247,161 inda ya kayar da sauran yan takara guda biyu.
Farfesa Ali Ibrahim Pantami ne yazo na biyu a zaɓen da kuri’a 12,120 sai kuma tsohon minista, Sa’idu Ahmad Alkali wanda ya samu kuri’a 11,612 inda ya zo na uku a zaɓen.

