Jami’ar Tarayya da ke Birnin Kebbi (FUBK) ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin ɗalibanta, Zaharadeen Nuhu, bayan wani hari da ake zargin wasu masu aikata laifi sun kai masa a wani masauki mai zaman kansa da ke Kalgo a Jihar Kebbi.
Marigayin, wanda ɗalibi ne a mataki na uku a sashen Kimiyyar Halittu (Biochemistry), ya samu munanan raunukan adda kuma ya rasu yayin da ake masa magani.
Shugaban Harkokin Ɗalibai na jami’ar, Farfesa Ibrahim Magawata, ya ce an sanar da Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya reshen Kalgo game da lamarin, kuma an fara bincike domin gano tare da cafke wadanda ke da hannu a harin.
Jami’ar ta ce an ƙara tsaurara matakan tsaro a Kalgo da sauran wuraren da ɗalibai ke zama a wajen harabar makaranta. Haka kuma, za ta gana da masu gidajen kwanan ɗalibai domin tattauna hanyoyin inganta tsaro.
An yi jana’izar marigayin ne a ranar Alhamis bayan sallar jana’iza da aka gudanar a masallacin Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Birnin Kebbi.
Jami’ar Tarayya Ta Birnin Kebbi Ta Tabbatar Da Rasuwar Ɗalibi Bayan Harin Yanta’adda

