Ƙungiyar dillalan mai ta IPMAN ta yi barazanar rufe gidajen mai a faɗin Najeriya idan gwamnatin tarayya ta tilasta musu sayar da man fetur a farashin da ta ƙayyade.
Barazanar ta biyo bayan gargaɗin da ƙaramin ministan albarkatun man fetur, Sanata Heineken Lokpobiri, da hukumar NMDPRA suka yi wa dillalan mai kan sayar da fetur a farashin da bai dace da saukar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya ba.
Sakataren yaɗa labarai na IPMAN, Chinedu Ukadike, ya ce ƙungiyar za ta dakatar da ayyukan gidajen mai idan gwamnati ta ƙaƙaba musu farashi.
A nata ɓangaren, hukumar NMDPRA ta ce za ta hukunta gidajen man da ke sayar da fetur fiye da yadda yanayin kasuwa ya tanada, tana mai cewa ana ci gaba da sa ido kan gidajen mai a faɗin ƙasar.
Ministan ya kuma bayyana cewa bayan sauyin da aka samu a rikicin Iran da Amurka, ƴan Najeriya na sa ran rage farashin man fetur.
IPMAN Ta Yi Barazanar Rufe Gidajen Mai Kan Ƙayyade Farashin Fetur

