INEC ta sanar da ranakun zabukan 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta sanar da ranakun da za a gudanar zabukan 2023.

Tun da farko dai hukumar ta sanar da cewa za a gudanar da zaben shugaban kasa ranar 23 ga watan Faburairu sai dai shugaban hukumar ta INEC, Mahmoud Yakubu ya fadawa yan jaridu cewa an sake saka sabbin ranakun zabe.

A cewarsa yanzu za a gudanar da zaben shugaban kasa da na yan majalisun tarayya ranar 25 ga watan Faburairu yayin da za a gudanar da zaben gwamnoni da na yan majalisun jiha ranar 11 ga watan Maris.

Sanar da ranakun zaben na zuwa ne kwana biyu bayan da shugaban kasa, Muhammad Buhari ya rattaba hannu kan sabuwar dokar zabe.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]