Hisbah Ta Kama Wani Mutum a Cikin Ghana-Must-Go a Gidan Matar Aure a Jihar Kebbi



Hukumar Hisbah ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum da ake zargin an same shi a ɓoye cikin jakar “Ghana Must-Go” a gidan wata matar aure da ke unguwar Badariya a Birnin Kebbi.

Daraktan Shari’a na hukumar, Sirajo Kamba, ya ce mazauna yankin ne suka sanar da Hisbah bayan sun ga mutumin ya shiga gidan matar da dare.

Ya bayyana cewa jami’an hukumar sun isa gidan bayan samun rahoto da misalin ƙarfe goma sha biyu da kwata na dare ranar Litinin. Da farko matar ta musanta cewa akwai wani mutum a cikin gidan, amma daga baya ta amince a gudanar da bincike.

Kamba ya ce jami’an sun gano mutumin a ɓoye cikin jaka, sannan binciken farko ya nuna akwai alaƙar soyayya tsakaninsa da matar auren.

A cewarsa, mutanen biyu sun amsa zargin yayin tambayoyi, kuma za a gurfanar da su bisa dokokin Musulunci.

More from this stream

Recomended