Akalla Falasdinawa 3 ne suka mutu yayin da wasu fiye da 20 suka jikkata a lokacin da wani jirgin leken asiri na Isra’ila ya kai harin bam a sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin da ke gabar yammacin kogin Jordan.
Majiyoyin tsaro da likitocin Falasdinu ne suka bayyana hakan a ranar Laraba, kamar yadda NAN ta ruwaito.
“An kai gawarwakin wasu matasa uku, tare da jikkata 20, wasu kuma na cikin mawuyacin hali, zuwa asibitin Jenin sakamakon harin da wani jirgin leken asiri na Isra’ila ya kai,” in ji Wissam Bakr, darektan asibitin gwamnati na Jenin.
Shaidun gani da ido na Falasdinawa sun ce dakaru masu yawa na Isra’ila sun kutsa kai cikin birnin Jenin, da kewayen sansanin, da kuma garin Burqin, a daidai lokacin da ake artabu da mayaĆ™an Falasdinu.