Harin Isra’ila ya halaka FalasÉ—inawa 3

Akalla Falasdinawa 3 ne suka mutu yayin da wasu fiye da 20 suka jikkata a lokacin da wani jirgin leken asiri na Isra’ila ya kai harin bam a sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin da ke gabar yammacin kogin Jordan.

Majiyoyin tsaro da likitocin Falasdinu ne suka bayyana hakan a ranar Laraba, kamar yadda NAN ta ruwaito.

“An kai gawarwakin wasu matasa uku, tare da jikkata 20, wasu kuma na cikin mawuyacin hali, zuwa asibitin Jenin sakamakon harin da wani jirgin leken asiri na Isra’ila ya kai,” in ji Wissam Bakr, darektan asibitin gwamnati na Jenin.

Shaidun gani da ido na Falasdinawa sun ce dakaru masu yawa na Isra’ila sun kutsa kai cikin birnin Jenin, da kewayen sansanin, da kuma garin Burqin, a daidai lokacin da ake artabu da mayaĆ™an Falasdinu.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...