Gwamnonin Yankin Igbo Sun Nesanta Kansu Da IPOB, Sun Zabi Zama A Najeriya – AREWA News


Gwamnonin sun kuma yi Allah wadai da hare-hare da kungiyar IPOB ke kaiwa da ya biyo bayan sake sabunta fafutukar neman shiyyar kudu ta bale dana Najeriya ta kasance kasa mai cin gashin kanta ta Biafra lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dukiyoyi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Shugaban kungiyar gwamnonin kudu maso gabas kuma gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi, ne ya bayyana hakan a madadin sauran takwarorinsa biyo bayan ganawa da suka yi a ranar Asabar domin neman mafita ga yanayin dardar da ake ciki na rashin tsaro tare da dawo da doka da oda da zaman lafiya a yankunan su.
Gwamnonin na kudu sun dora alhakin dukannin hare-haren baya-bayan nan da aka yi ta kaiwa kan ofisoshin jami’an tsaro da gine-ginen gwamnati a yankunan kudu maso gabas akan kungiyar ta IPOB.

Shugaba Buhari (hagu) da gwamnan Ebonyi David Umahi yayin wata ziyara da kai wa Abuja (Facebook/David Umahi)
Shugaba Buhari (hagu) da gwamnan Ebonyi David Umahi yayin wata ziyara da kai wa Abuja (Facebook/David Umahi)

A wata hira da ya yi da manema labarai makonni biyu da suka gabata, tsohon gwamnan Imo Sanata Rochas Okorocha, ya ce dattawa yankin suna yin shiru ne saboda gudun kada a kai wa iyalansu hari.
Sai gwamna Umahi ya ce babu kamshin gaskiya a cikin zarge-zargen cewa, sun yi shiru kan lamarin da ke faruwa a yankunansu yana mai cewa ba sa goyon bayan matasan da ke wannan fafutuka, ya na mai cewa, ‘yan kungiyar IPOB ba su da hurumin yin magana a madadin ‘yan kudu.
Haka kuma, gwamna Umahi, shugabannin yankunan kudu sun kafa kwamiti da zai shiga tsakani da matasan masu fafutukar neman balewa don fahimtar da su kan duk abin da ke ci musu tuwo a kwarya.

Gwamnonin jam'iyyar APC bayan wani taro da suka yi (Facebook/David Umahi)
Gwamnonin jam’iyyar APC bayan wani taro da suka yi (Facebook/David Umahi)

Daga karshe, gwamnonin sun bukaci hukumomin tsaro a yankin su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu kamar yadda dokar kasar ta tanadar tare da mika bukatar mambobin majalisun kasar daga yankin, su mara baya ga batun kafa ‘yan sandan jiha a aikin gyara kundin tsarin mulki da su ke aiki a kai a halin yanzu.
Idan ana iya tunawa, a shekarar 2012 ne kungiyar IPOB ta fara fafutukar balewa daga kasar inda gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana kungiyar a matsayin haramtaciyya bayan wasu taho-mu-gama da jami’an soji a yankunan kudu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...