Gwamnan Taraba Ya Durkusa Har Ƙasa Ya Na Neman Al’umma Su Yafe Masa

Gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku ya nemi afuwar mutanen Taraba h waɗanda ya batawa a tsawon wa’adinsa na shekara 8.

Ishaku ya nemi ayi masa afuwa ne yayin taron addu’ar nuna godiya da kungiyar Kiristoci ta CAN reshen jihar Taraba ta shirya a hedkwatar ta dake Jalingo.

Gwamnan ya ce yayi murna cewa takensa na ” Ku bani Zaman Lafiya Ni Kuma Zan Kawo Muku Ayyukan Cigaba.” ya samu wurin zama a zukatan al’ummar jihar.

Tun da farko Ishaku a wurin taron addu’o’in Bikin Ista na musamman da aka gudanar a Cocin Anglican dake Mayo Dosa a Jalingo ya durkusa har ƙasa a gaban mahalarta taron inda ya nemi gafarar mutanen da ya batawa a cikin shekaru 8 na mulkinsa.

Za a iya cewa Gwamna Ishaku ya bi sawun shugaban kasa Muhammad Buhari da kuma gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje da suka nemi jama’a su ya fesu

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]