FIFA da NFF sun ƙaddamar da ƙaramin filin wasa a jihar Kebbi

Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA da kuma hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya NFF sun ƙaddamar da wani f ƙaramin filin wasa a jihar Kebbi.

A ƙalla dalar Amurka miliyan 1.19 aka kashe wajen samar da filin wasan.

A cewar kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN gwamnan jihar, Nasir Idris shi ne ya jagoranci bikin kaddamar da filin wasan dake kan titin Kalgo a birnin Kebbi.

A cikin watan Satumba na shekarar 2020 tsohon gwamnan jihar,Atiku Bagudu ya aza harsashin ginin filin wasan.

Da yake magana a wurin bikin shugaban hukumar NFF, Ibrahim Gusau ya ce hukumar za ta cigaba da samar da sauran kayayyaki a filin domin daga darajarsa a nan gaba.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...