Fadar Shugaban Ƙasa Ta Zargi Peter Obi Da Ƙirƙirar Labarai Domin Neman A Tausaya Masa



Mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya ce tsohon gwamnan jihar Anambra kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, yana ƙirƙirar labarai ne domin jawo masa tausayin jama’a.

Onanuga ya bayyana haka ne bayan Peter Obi ya yi ikirarin cewa yana fargabar ko zai kai ga zaɓen shekarar 2027 da ransa, tare da zargin gwamnatin tarayya da hana shi gudanar da harkokinsa.

Sai dai Onanuga ya ce waɗannan zarge-zarge ba su da hujja, yana mai cewa Shugaba Bola Tinubu yana mai da hankali kan ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki, kuma ba shi da lokacin mayar da martani ga abin da ya kira ikirarin da ba su da tushe.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]