Dani Alves zai saka riga mai lamba 8 a Barcelona

Dani Alves

Asalin hoton, Barcelona FC

Barcelona ta gabatar da Dani Alves a matakin sabon dan wasanta ranar Laraba a Camp Nou.

An gabatar da shi a gaban magoya baya 10,000 daga nan kuma ya gana da ‘yan jarida, bayan bikin gabatar da shi da jawabai.

Dan wasan tawagar Brazil zai yi wa Barcelona tamaula a karo na biyu, zai kuma sa riga mai lamba takwas, irin wadda ya yi amfani da ita Sevilla.

Wannan shine karo na biyar da Alves zai saka riga mai lamba daban-daban a kungiyar, bayan da zai buga mata tamaula a karo na biyu.

Daga cikin wadanda suka yi amfani da lamba takwas a Barcelona sun hada da Andres Iniesta da Ludovic Giuly da Hristo Stoichkov da kuma Guillermo Amor da Albert Celades da Phillip Cocu da Arthur Melo da kuma Miralem Pjanic.

Alves ya fara sa riga mai lamba 20 a karon farko da ya je Barcelona a 2008, bayan kaka hudu ya koma saka lamba biyu, sannan ya karbi lamba 22 don girmama abokin taka ledarsa Eric Abidal.

Ya kuma sa riga mai lamba shida, bayan da Xavi Hernandez ya bar Barcelona, wanda yanzu ke horar da kungiyar ta Camp Nou.

Alves ya fara atisaye a Barcelona tun daga Litinin, amma ba zai buga wa kungiyar gasa ba har sai watan Janairun 2022.

(BBC Hausa)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...