Dani Alves zai bar Paris St-Germain | BBC news

Copa America

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Dani Alves zai bar Paris St-Germain, bayan kaka biyu da ya yi a kungiyar da ke buga gasar lik ta Faransa.

Dan wasan tawagar kwallon kafar Brazil, mai shekara 36 ya ci kwallo uku a wasa 73 da ya buga wa PSG, tun komawarsa Faransa daga Juventus a 2017.

Tsohon dan wasan Sevilla da Barcelona ya ci wa Brazil kwallo a wasan da suka yi nasarar doke Peru 5-0 a gasar Copa America ranar Asabar.

Alves ya ci kofin Ligue 1 biyu a jere da Coupe de France da kuma Coupe de Ligue.

Bayan da mai tsaron bayan ya yi shekara daya a Juventus kafin ya koma PSG, ya lashe La Liga shida da Champions League uku a Barcelona.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]