Dani Alves zai bar Paris St-Germain | BBC news

Copa America

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Dani Alves zai bar Paris St-Germain, bayan kaka biyu da ya yi a kungiyar da ke buga gasar lik ta Faransa.

Dan wasan tawagar kwallon kafar Brazil, mai shekara 36 ya ci kwallo uku a wasa 73 da ya buga wa PSG, tun komawarsa Faransa daga Juventus a 2017.

Tsohon dan wasan Sevilla da Barcelona ya ci wa Brazil kwallo a wasan da suka yi nasarar doke Peru 5-0 a gasar Copa America ranar Asabar.

Alves ya ci kofin Ligue 1 biyu a jere da Coupe de France da kuma Coupe de Ligue.

Bayan da mai tsaron bayan ya yi shekara daya a Juventus kafin ya koma PSG, ya lashe La Liga shida da Champions League uku a Barcelona.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...