Dani Alves zai bar Paris St-Germain, bayan kaka biyu da ya yi a kungiyar da ke buga gasar lik ta Faransa.
Dan wasan tawagar kwallon kafar Brazil, mai shekara 36 ya ci kwallo uku a wasa 73 da ya buga wa PSG, tun komawarsa Faransa daga Juventus a 2017.
Tsohon dan wasan Sevilla da Barcelona ya ci wa Brazil kwallo a wasan da suka yi nasarar doke Peru 5-0 a gasar Copa America ranar Asabar.
Alves ya ci kofin Ligue 1 biyu a jere da Coupe de France da kuma Coupe de Ligue.
Bayan da mai tsaron bayan ya yi shekara daya a Juventus kafin ya koma PSG, ya lashe La Liga shida da Champions League uku a Barcelona.