Champions League: Sau nawa PSG da Real Madrid suka kara

Benzema Neymar

Asalin hoton, Getty Images

Paris St Germain za ta fafata da Real Madrid a wasan zagaye na biyu a Champions League, bayan da aka raba jadawali ranar Litinin.

Za su fara buga wasan farko a tsakaninsu a birnin Paris ranar 15 ga watan Fabrairu, sannan karawa ta biyu a yi a Santiago Bernabeu ranar 9 ga watan Maris.

An kara tsakanin PSG da Real Madrid sau shida, inda Real ta yi nasara a wasa uku da canjaras biyu, inda kungiyar Faransa ta yi nasara daya.

Fafatawar da aka yi tsakanin PSG da Real Madrid:

Champions League ranar Talata 26 ga watan Nuwambar 2019

  • Real Madrid 2 – 2 Paris St-Germain

Champions League ranar Laraba 18 ga watan Satumbar 2019

  • Paris St-Germain 3 – 0 Real Madrid

Champions League ranar Talata 6 ga watan Maris 2018

  • Paris St-Germain 1 – 2 Real Madrid

Champions League ranar Laraba 14 ga watan Fabrairun 2018

  • Real Madrid 3 – 1 Paris St-Germain

Champions League ranar Talata 3 ga watan Nuwambar 2015

  • Real Madrid 1 – 0 Paris St-Germain

Champions League ranar Laraba 21 ga watan Oktobar 2015

  • Paris St-Germain 0 – 0 Real Madrid

Yadda aka raba jadawalin Champions League:

  • Salzburg da Bayern Munich
  • Sporting da Manchester City
  • Benfica da Ajax
  • Chelsea da Lille
  • Atletico da Manchester United
  • Villarreal da Juventus
  • Inter da Liverpool
  • PSG da Real Madrid

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...