Manchester City ta ziyarci Paris St Germain, domin buga wasa na biyu na cikin rukuni a Champions League ranar Talata.
Wannan shine wasa na shida da kungiyoyin biyu za su fafata a gasar ta kofin Zakarun Turai, inda City ta ci karawa uku da canjaras biyu.
City ce ta doke PSG 4-1 gida da waje a wasan daf da karshe a bara a gasar ta Zakarun Turai,
Kungiyoyi biyun za su buga wasannin da kwarin gwiwa, bayan da PSG ke kan teburin Ligue 1 da cin dukkan wasanninta takwas a kakar bana, ita kuwa Manchester City ta je Stamford Bridge ta doke Chelsea a gasar Premier League ranar Asabar.
Sai dai PSG bata ci wasa ba a karawa hudu a Champions League, tun bayan canjaras da Club Bruges a wasan zagayen farko.
City ta casa RB Leipzig 6-3 a gida a wasan farko a cikin rukuni a bana, kuma ta yi karawa 10 ba tare da an doke ta ba a Champions League.
Wasanni biyar baya da suka kara tsakanin PSG da City:
Champions League Talata 4 ga watan Mayun 2021
- Man City 2 – 0 Paris St-Germain
Champions League Ranar Laraba 28 ga watan Afirilun 2021
- Paris St-Germain 1 – 2 Man City
Champions League Ranar Talata 12 ga watan Afirilun 2016
- Man City 1 – 0 Paris St-Germain
Champions League Ranar Laraba 6 ga watan Afirilun 2016
- Paris St-Germain 2 – 2 Man City
UEFA CUP Ranar Laraba ga watan Disambar 2008
- Man City 0 – 0 Paris St-Germain
‘Yan wasan PSG da za su kara da Man City:
28.Eric Junior Dina Ebimbe
PSG ta bayyana Messi cikin wadanda za su fafata da City a Faransa, karon farko da zai buga Champions League a kungiyar, wanda bai yi mata wasa biyu a League 1, sakamakon jinya da ya yi.
Kyaftin din Argentina, wanda ya taka leda karkashin Pep Guardiola a Barcelona bai ci kwallo ba har yanzu a wasa uku da ya buga wa sabuwar kungiyarsa.
Messi shine kan gaba da ya ci Manchester City kwallaye da yawa – wanda ya zura shida a wasa hudu, har da guda hudun da ya ci City a karawa da Barcelona da biyu a lokacin da kocin yake Bayern Munich.
(BBC Hausa)