Da gaske ne gwamnatin Rivers ta rushe masallaci? BBC Hausa

Vacant land

Image caption

Mutanen da suke zaune a yankin da abin ya faru sun shaida wa BBC cewa an yi rusau din ne makon da ya gabata

Gwamnan jihar Rivers a Najeriya, Govnor Nyesom Wike ya musanta rahotannin da ke cewa gwamnatinsa ta rushe wani masallaci a jihar.

Gwamna Nyeson Wike ya shaida wa ‘yan jaridu cewa gwamnatin ta hana masu son gina masallacin yin gini, inda mutanen suka je kotu amma kuma gwamnati ta samu nasara a kansu.

A ranar Juma’a ne dai wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta ya nuna taron masallata na sallar Juma’a a wani wurin da aka rushe da aka ce wani masallaci ne da gwamnatin jihar Rivers ta rushe da ke yankin Trans Amadi na birnin Port Harcourt.

Wannan batu dai ya janyo ka ce-na ce da tayar da jijiyoyin wuya a kafafen sada zumunta musamman tsakanin al’ummar kudu da arewa ko kuma tsakanin musulmi da kiristoci.

  • Hotuna: Sultan Abubakar Saad III ya girmama Gwamna Wike na jihar Rivers
  • Nigeria: An kashe mutum 21 a jihar Rivers

Gwamna Wike ya ce “Abun takaici ne a ce mutanen suna tunanin cewa sun gina masallaci amma gwamnati ta rushe musu”.

Babban limamin masallacin na Trans Amadi, Alhaji Harun Mohammad, ya shaida wa sashen BBC na Broka cewa a 2010 ma gwamnati ta rushe masallacin ba tare da ba su wa’adi ba.

Ya kara da cewa sun kai gwamnatin gaban kuliya inda kotun ta damka musu filin kuma daga nan ne suka fara gina masallacin, kwatsam sai ga shi gwamnati ta sake rushe musu.

Mazauna yankin Rainbow na birnin Port Harcourt sun shaida wa BBC cewa a makon da ya gabata ne dai aka gudanar da rusau din.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...