Coronavirus: Miliyoyin mutane sun rasa damar samun aiki ta shafin LinkedIn

Linkedin

Miliyoyin mutane a sassan duniya sun rasa ayyukansu saboda barkewar annobar korona.

Wata sabuwar kididdiga da manhajar LinkedIn mai samar da ayyukanyi ta Amurka ta fitar ta nuna cewa yawancin tattalin arzikin kasashen duniya na kokarin farfadowa daga durkushewar da ya shiga bayan bullar cutar korona ga kuma matsalar rasa ayyukan yi ta annobar ta haifar.

A yanzu haka kasashen da dama a duniya na kokarin farfado da tattalin arzikinsu da kuma mayar da mutane kan ayyukansu da suka rasa bayan bullar annobar koorna.

Kididdigar ta manhajar Linkedin ta fitar bayan tattara bayanai daga kasashe 15 ya nuna cewa kasashen ba zasu iya ciki gibin ayyukan da suka rasa ba.

Kididdigar ta kuma nuna cewa kasashen turai da Amurka sun gaza cike gibin ayyukan da suka rasa da kaso 50 cikin 100 idan aka kwatanta da bara kamar a yanzu,

Kasashen nahiyar Asiya su da dan dama-dama a cewar kididdigar manhajar ta Linkedin saboda sassauta dokokin kullen da suka yi ya sa al’amuran kasuwanci a kasashen sun dan inganta.

To amma kididdiga daga Sweden da Brazil ta nuna cewa duk da biris din da aka yi da dokar kulle a kasashen hakan bai cimma ruwa ba.

To sai dai kuma kididdigar ta nuna cewa ana samun ci gaba ta fuskar daukar ma’aikata ko samar da aikin yi ga jama’a a wasu yankuna na China da Faransa da kuma Canada.

Kazalika fargabar da ake da ita ta sake barkewar cutar korona a karo na biyu ya tsayar da daukar sabbin ayyuka a wasu kasashe da daman a duniya.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...