BBC Hausa: Mu na neman afuwan ‘yan Najeriya kan karancin man fetur – NNPC

Mele Kyari

Asalin hoton, MELEKYARI/NNPC

Shugaban Kamfanin mai na kasa, NNPC ya bai wa ‘yan Najeriya hakuri kan matsin da suka sake tsintar kansu sakamakon karancin man fetur.

Shugaban kamfanin man, Mele Kolo Kyari ya tabbatar wa BBC cewa ana sa ran matsalar ta yanke cikin ƴan kwanaki kaɗan masu zuwa.

Kalaman Mele Kyari a tattaunawar sa da BBC, na zuwa ne a daidai lokacin da al’umma a Najeriya ke ci gaba da fuskantar dogayen layukan mai, musamman a manyan biranen ƙasar.

Matsalar ta man fetur, wadda ta ƙi ci ta ƙi cinyewa tun a shekarar da ta gabata, na ci gaba da jefa al’ummar Najeriya cikin garari, yayin da babban zaɓen ƙasar ke ƙaratowa.

Sai dai Mele Kyari ya ce cikin kwanaki biyu masu zuwa za a samu sauki ko da wahalar bata kare ba baki ɗaya domin hukumomi sun ɗauki matakan da suka dace domin ganin an shawo kan matsalar.

Wasu labaran masu alaƙa da za a iya karantawa

Me ya sa aka gagara shawo kan matsalar?

Malam Mele Kyari ya shaida cewa, dama duk lokacin da aka samu tangarɗa wajen raba fetur ana shiga cikin irin wannan yanayi, kuma a kan ɗau tsawon lokaci kafin a warware.

Mele ya ce suna da tarin mai jibge a kasa wanda za a iya shafe kwanaki 30 ba tare da an wahala ba.

Sai dai tangarɗan da aka samu wanda ya kai ga mutane sun shiga gidan mai suna sayen mai fiye da bukatarsa, shi ke haifar da dogayen layuka.

Sannan ya ce akwai matsaloli kamar ta dauko man daga manyan jirage da ke kan ruwa zuwa defo-defo, kana a kai su gidajen mai.

Sai dai canje-canjen farashi a kasuwar duniya ya shafi wasu ayyukansu.

Mele ya ce wannan ne dalili ya sa idan ‘yan kasuwa sun dauko man ba zai yiwuwa ba, su zo su sayar da shi a yadda gwamnati ta kayyade, wannan shi ne dalilin wahalar feturin.

‘Wasu gidajen mai na nuna haɗama’

Shugaban NNPC ya kuma sake fito da wani batun na yadda wasu gidajen man ke nuna haɗama da tsawala farashin fetur da yawa, yana mai cewa hukumomin da alhakin daidaita farashi ke kan su na bibbiyar lamarin domin shawo kan matsalar.

Malam Mele ya ce sun dau matakan ganin fetur ya wadatu a kasuwa ta hanyar zama da ‘yan kasuwa da abin ya shafa domin tabbatar da cewa man na isa ga manyan biranen Najeriya.

Sannan a wasu wuraren kamar Abuja ana haɗawa da jami’an tsaro domin ganin man ya wadatu ba tare da an boye ba.

Shugaban ya bai wa ‘yan Najeriya hakuri tare da alkawarta cewa nan bada jimawa ba komai zai daidaita, sauki sai samu a sassan kasar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...