Bai kamata Buhari ya yi shiru kan rikicin Kano ba – Bafarawa

Sarki Sanusi

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

—BBC Hausa

Wani jagoran al’umma a yankin arewacin Najeriya ya soki lamirin manyan mutanen yankin da yin shiru game da rikicin masarautar Kano, wanda ya ce yana iya shafar daukacin kasar gaba daya.

“Wannan rigima da ake Kano, ba rigimar Kano ba ce, rigima ce ta arewa, kuma ba rigimar arewa ba ce, rigima ce ta Najeriya, in ji Alhaji Dalhatu Attahiru Bafarawa.

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, ya ce: “Saboda irin wadannan manyan mutane suna rigima, a ce ba wani wanda ya isa ya fito cikin dattijan arewa, irin sarakunanmu, Sarkin Musulmi da Sarkin Zazzau da Shehu Borno, manyan sarakunanmu da malamanmu…”

Rikicin ya shafi gididdiba masarautar Kano zuwa gida biyar tare da binciken fadar sarkin Kano da gwamnatin jihar ke yi a kan wasu biliyoyin kudaden da ake zargin masarautar ta kashe ba bisa ka’ida ba.

Bafarawa ya ce abin kunya ne a ce Kayode Fayemi, gwamnan jihar Ekiti, shi ne zai zo ya jagoranci sulhunta Sarkin Kano da gwamnan jihar.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Ya ce a ra’ayinsa maganar shugaban gwamnonin Najeriya (wanda Kayode Fayemi yake jagoranta) ba ta ma taso ba.

“Ai maganar karkashin kasa ba taso ba, tun da abu ya hito hili, ya kamata kowa a zo a ga mai ya ce,” in ji Bafarawa.

A cewarsa: “Ina Sarkin Muslmi? Ina Sarkin Zazzau? Ina Shehun Borno? Wannan wata matafiya ce aka taba, wanda ya shafi wadannan mutane. Muna da mallamai, mallamai suna hakkin su zo su yi nasiha ga wadannan mutane.”

Tsohon gwamnan ya ce kamata ya yi dattijan arewa su hadu a matsayin kwamiti wanda zai kunshi manyan mutane da malamai da masarautu da ‘yan kasuwa.

“Shi ma kansa, uban tafiyar, ubanmu shugabanmu, Muhammadu Buhari, bai kamata ba ya zura ido ana wannan abu.” a cewar fitaccen dan siyasar.

Bafarawa ya ce a yau idan Buhari ya kirawo su, ya tsawatar (magana ta mutu) ba sai ya sa kowa ba, “ubanmu ne, shugabanmu ne, shi as shugabanmu a arewa yau”.

An tambayi Dalhatu Bafarawa wanda a lokacin mulkinsa ne aka nada Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III, ko a ganinsa me ke kawo irin wannan rikici? Sai ya ce yana ganin shaidan ne.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...